فهرست کتاب‌‌ لیست کتاب‌ها
■ SADAUKARWA
■ GABATARWA
■ FASALI NA 1
■ WANE NE MAI TARBIYA ?
■ KASHE-KASHEN TARBIYA
■ ABUBUWAN DA SUKA RATAYU DA ITA
■ IYALI CIKIN MA'ANAR LUGGA DA ISDILAHI
■ IYALI A LUGGANCE
■ FASALI NA 2
■ AUREN DABI'A
■ AUREN SHARI'A
■ KASHE-KASHEN AURE
■ ADADIN MAZAJE
■ HANYOYIN TABBATAR AURE
■ kasantuwan miji daya rak mace daya rak
■ FASALI NA 3
■ DALILAN DAKE SANYA YIN AURE DA MANUFOFINSA
■ SAMUN CIKAR KAMALA CIKIN AURE
■ DALILAN YIN AURE CIKIN SUNNA MAI DARAJA
■ TAUHIDI
■ TAKAWA
■ MAFI SOYUWAR GINI WAJEN ALLAH
■ SUNNAR ANNABI
■ KARUWAR ARZIKI
■ KARUWAR IMANI
■ ALFAHARI
■ KARUWAR IBADA
■ GARKUWA
■ SADAR DA ZUMUNCI
■ RIKO DA ADDINI
■ DEBE HASO
■ FASALI NA 4
■ DALILAN TARBIYA NA GADO DA DABI'A CIKIN AURE
■ ASALI
■ WATA CIKIN BURUJIN AKRABU
■ HUKUNCIN ILIMIN BUGA KASA CIKIN SHARI'A MAI TSARKI
■ MAHALLIN DA MUTUM KE RAYUWA CIKI
■ SON MATA
■ MATA MASU MUTUNCI DA DARAJA
■ 1MATAYE MAFI KYAWUN FUSKOKI MAFI KARANCI SADAKI
■ KARANCIN BUKATU DA SAUKAKE HAIHUWA
■ KASHE-KASHEN MATA CIKIN KYAWAWAN HALINSU
■ TSARA CIKIN AURE
■ FASALI NA 5
■ YARDA SHARADI NE CIKIN AURE
■ FAFUTIKA CIKIN AURE
■ AUREN WURI
■ HUDUBA
■ SADAKI
■ HATSARIN TSADAR SADAKI
■ AUREN SHARI'A
■ DAREN ANGONCI
■ KABBARA
■ AYYUKAN DAREN ANGONCI
■ ZAMA TARE DA AMARYA HAR TSAWON KWANAKI BAKWAI
■ WALIMA
■ RARRABA ALEWA KO DABINO
■ LADUBBAN SADUWA DA IYALI
■ MAFI DADIN DADADA
■ WASA DA MATA GABANIN JIMA'I
■ LOKUTAN SADUWA NA MUSTAHABBI DA NA MAKARUHI
■ HUKUNCIN AZALO
■ ADDU'A YAYIN KUSANTAR IYALI
■ FASALI NA 6
■ HAKKOKIN DA MA'AURATA SU KAYI TARAYYA CIKI
■ HAKURI
■ KAMEWA DAGA ZALUNCI DA CUATARWA
■ HAKKOKIN MACE
■ CIYARWA DA YALWATAWA
■ TAUSAYAWA DA KAMEWA DAGA ZALUNCI
■ KAMEWA DAGA BARIN DUKA MAI CUTARWA
■ UMARNI DA KYAKKYAWA DA HANI DA MUMMUNA
■ GARKUWA
■ KYAUTATAWA
■ KYAWUNTA ZAMANTAKEWA
■ KYAWUNTA ZAMANTAKEWA
■ HAKKOKIN MIJI
■ NEMAN IZINI CIKIN AIKI DA TASARRUFI
■ TAUSAYAWA MIJI
■ HIMMATUWA DA KULA DA CIKIN GIDA DA KAYAYYAKINSA
■ HIMMATUWA CIKIN SAUKE HAKKOKI
■ JIMA'I
■ ADO
■ KAMEWA CIKIN MAGANA
■ MAZAJE SUNE MASU TSAYUWA
■ SHUGABANTAR IYALI
■ DALILAI DA SUKE SANYA DAWWAMAR AURE
■ SON JUNA
■ YAWAITA AIKATA ALHERI
■ SANYA FARIN CIKI
■ BIYAYYA DA NEMAN YARDAR MIJI
■ KIYAYE MUTUNCI DA DUKIYA
■ TAIMAKO DA TALLAFAWA
■ TARBAR MIJI DA KYAWUNTA BANKWANA DA SALLAMA
■ KALAMIN AKIDOJI MAI KYAWU DA KARFAFAFFEN FURUCI
■ KARBAR UZURI DA YIWA JUNA UZURI
■ BINSU SANNU SANNU CIKIN KOWANNE HALI
■ KYAWUNTA LAFAZI CIKN KOWANNE YANAYI
■ RASHIN SAURARON KYAUTATA AIKI DARI BISA DARI
■ RASHIN IKON DAUKAR NAUYI A RAYUWANCE
■ RASHIN GORI KAN MIJI
■ RASHIN KAURACEWA AL'AMARIN SHIMFIDA
■ YIN SHAWARA DA MATA AMMA BANDA BIYE MUSU
■ TAKA TSAN TSAN DA KUMA FARKAWA
■ HANKALTA
■ MIJI SHI NE MUTUNCIN MATARSA
■ KISHI
■ TAIMAKEKENIYYA
■ DADADAWA IYALI
■ TAFIYAR DA GIDA NA HANNUN MIJI.
■ BOYEWA MATA HARKOKIN KUDADENKA
■ KYAWUNTA ZAMA DA MIJI
■ WATSI DA BOKANCI DA TSAFE TSAFE
■ HIDIMA MADAWWAMIYA
■ GODIYA
■ KAUNAR JUNA
■ TSINTUWA GUDA BIYU GIDAN ALI DA FATIMA
■ FASALI NA 7
■ MUKAMI NA FARKO
■ SON `YA`YA DA KANAN YARA
■ MUKAMI NA 2
■ DA NAMIJI KO MACE
■ MUKAMI NA 3
■ NEMAN HAIHUWAR DA NAMIJI
■ MUKAMI NA 4
■ RAINON CIKI DA LADUBBNSA
■ MUKAMI NA 5
■ TASIRIN ABINCI KAN MATA MASU CIKI DA YARA DA JIMA'I
■ MUKAMI NA 6
■ HAIHUWA
■ MUKAMI NA 7
■ SHAYARWA
■ MUKAMI NA 8
■ RADIN SUNA
■ MUKAMI NA 9
■ TAYA MURNA DA SAMUN `DA
■ MUKAMI NA 10
■ AKIKA
■ WASU AYYUKAN MUSTAHABBAN NA DABAN
■ MUKAMI NA 11
■ KACIYA
■ MUKAMI NA 12
■ KAMANCECENIYARSA DA MAHAIFINSA
■ MUKAMI NA 13
■ MATAKAN TARBIYYYAR YARA
■ MUKAMI NA 14
■ ADALCI TSAKANIN `YA`YA
■ MUKAMI NA 15
■ SUMBATA NA DAGA ALAMOMIN SO
■ FASALI NA 8
■ HUKUNCE HUKUCEN MATA DA YARA
■ FASALI NA 9
■ BATUTUWA DABAN-DABAN
■ FASALI 10
■ SAKI
■ GABATARWA
■ HAKIKANIN LADABI KAN HASKEN MAZHABAR IYALN GIDAN ANNABI
■ WAYE ME LADABTARWA
■ ME NENE LADABI
■ ASALAN LADUBBA
■ MASADIR CIKIN LADUBBA
■ MASADIR DIN LARABCI
■ SUNAN LITTTAFI DA SUNAN MARUBUCINSA

RADIN SUNA

 

daga cikin al'amuran da muslunci ya yi ishara gare su shi ne batun radin suna da abin da yak e tattate da shi daga tasiri mai girma a rai da shi kansa mutuncin yaron.

wasu cikin mutanen yammacin turai da gabashinta na ladubba cikin radin suna sukan shirya biki dukkanin makusantan miji da mata su hadu don zabar suna ga yaron da aka haifa musammam dan fari.

hakika muslunci ya himmatu da batun radin suna, lalle suanye suna sauka daga sama, ta ba da labarin abubuwan boye sannan shi suna na dangantaka da mai suna, kamar yadda ma'abota munanan sunaye za ka samu da yawan lokuta suna jin kunya yayin da aka kiraye su da wadannan sunaye, haka al'amarin ya ke cikin lakabi da alkunya.  ta nan ne ya kasance da na da hakkin ubansa ya  zaba masa kyakkyawan suna, idan bai zabar masa kyakkyawan sun aba to ya takaita cikin sauke hakkinsa kuma ya wulakanta dansa, sannan shi mai sabawa da wulakanta dansa ya yi nesa da rahamar Allah matsarkaki.

عن النبيّ (صلى الله عليه وآله) ، قال  : من حقّ الولد على والده ثلاثة  : يحسن اسمه ، ويعلّمه الكتابة ، ويزوّجه إذا بلغ .

1 – annabi (saw) ya ce: daga hakkin da kan ubansa  abubuwa uku : kyawunta sunansa, ya koya masa rubutu, ya aurar da shi idan ya balaga.

وقال (صلى الله عليه وآله)  : سمّوا أولادكم أسماء الأنبياء ، وأحسن الأسماء عبد الله وعبد الرحمن

2 – manzon Allah (saw) y ace : ku radawa `ya`yanku suna annabawa mafi kyawun sunaye su ne Abdullah abdur-rahman.

الكافي بسنده ، عن أبي بصير ، عن أبي عبد الله (عليه السلام) ، قال  : حدّثني أبي عن جدّي ، قال  : قال أمير المؤمنين (عليه السلام)  : سمّوا أولادكم قبل أن يولدوا فإن لم  تدروا أذكر أم اُنثى فسمّوهم بالأسماء التي تكون للذكر والاُنثى ، فإنّ أسقاطكم إذا لقوكم يوم القيامة ولم تسمّوهم يقول السقط لأبيه  : ألا سمّيتني وقد سمّى رسول  الله (صلى الله عليه وآله) محسناً قبل أن يولد

3 – alkafi da isnadinsa daga baban basiru daga baban abdullah (as) ya ce : babana ya zantar da ni daga kakana, ya ce: sarkin muminai ali (as) ya ce: ku radawa `ya`yanku sunaye tun gabanin haihuwarsu idan ba ku san cewa mace ne ko namiji to rada musu sunan da daukar mace da namiji, lalle `ya`yanku da aka yi barinsu idan suka hadu da ku ranar alkiyama alhalin ba ku rada musu suna ba sai dan da kayi barinsa ya cewa mahaifinsa yanzu b aka radan suna bayan manzon Allah (saw) ya radawa muhsin dan fatima suna gabanin haihuwarsa.

muhsin shi da ne ga Fatima azzahara (as)  shugabar matan duniya wanda ta yi barinsa sakamakon buga mata kyauren kofa da wani wanda Kalmar azaba ta tabbata kansa ya yi.[1]

Bayani kan dan Fatima(as) mai suna muhassin wanda ta yi barinta sakamkon dukan wanda zabar Allah ta gasgata kansa ya yi mata

عن أبي الحسن الأوّل (عليه السلام) قال  : أوّل ما يبرز الرجل ولده أن يسمّيه باسم حسن فليحسن أحدكم اسم ولده

4-daga baban Hassan(as) ya ce: farkon abin da mutum zai fara yayinda aka Haifa masa da shine ya sanya masa suna mai kyawu, dayanku ya kyawunta sunan dansa.

1-      عن أبي عبد الله (عليه السلام)  : لا يولد لنا ولد إلاّ سمّيناه محمّداً ، فإذا مضی سبعة أيام فإن شئنا غيّرنا وإن شئنا تركنا

5 – an karbo daga baban abdullah (as) ba za'a Haifa mana d aba face mun sanya masa suan muhammadu idan kwanaki bakwai suka shude idan muka so sai mu sauya ko kuma mu bar masa wannan suna

عن أبي عبد الله (عليه السلام) قال  : إنّ النبيّ (صلى الله عليه وآله) قال  : من ولد له أربعة أولاد لم  يسمّ أحدهم باسمي فقد جفاني

6– an karbo daga baban Abdullah (as) ya ce: manzon Allah (saw) ya ce : duk wanda aka haifa masa `ya`ya hudu bai sanyawa dayansu sunan muhammadu ba hakika ya yi mini jafa'i.

الكافي عن العرزمي قال  : استعمل معاوية مروان بن الحكم على المدينة وأمره أن يفرض لشباب قريش ففرض لهم فقال عليّ بن الحسين (عليهما السلام)فأتيته فقال  : ما اسمك  ؟ فقلت  : عليّ بن الحسين . فقال  : وما اسم أخيك  ؟ فقلت  : عليّ . فقال  : ثمّ فرض لي فرجعت إلى أبي فأخبرته فقال  : ويل على ابن الزرقاء دبّاغة الأدم ، لو ولد لي مئة لأحببت أن لا اُسمّي أحداً منهم إلاّ عليّاً

7 – alkafi daga azurmi ya ce: mu'awiya ya sanya marwanu gwamna a madina ya umarce shi ya farlanta farilla kan matasan madina sai na je wajensa sai y ace mini meye sunanka sai n ace masa aliyu dan husaini, y ace meye sunan dan'uwanka na ce: ali sannan nima ya bani sai na dawo wajen babana na bashi labari sai ya ce: azaba ta tabbata kan dan shudiya ma'bocin jemammiyar fata, da za'a haifa mini `ya`ya dari da na kaunaci radawa dukkaninsu suna aliyu.

عن الجعفري قال  : سمعت أبا الحسن (عليه السلام) يقول  : لا يدخل الفقر بيتاً فيه اسم محمّد أو أحمد أو علي أو الحسن أو الحسين أو جعفر أو طالب أو عبد الله أو فاطمة من النساء صلّى الله عليهم

7 – daga jafari ya ce: na ji baban hassan (as) ya na cewa: talauci bai shiga gidan da yake da yaro mai suna muhammadu ko ali ko ahmad ko hassan ko husaini ko kuma jafar da dalib da Abdullah daga cikin mata kuma fatima 

da wadannan sunaye masu albarka a'imma (as) suka nufi raya al'arain wadannan manyan mutane, da raya mazahabarsu ta gaskiya wadanannan mutane suna ishara gareta, ya kamata duk wani dan shi'a ya zabi wadannan sunaye saboda lalle akwai albarka da wadata tattare da su, kamar yadda cikinsu akwai raya mazhabar iyalan annabi (saw).

عن أبي عبد الله (عليه السلام) قال  : جاء رجل إلى رسول الله (صلى الله عليه وآله) فقال  : يا  رسول الله ، ولد لي غلام فماذا اُسمّيه  ؟ قال  : سمّه بأحبّ الأسماء إليّ حمزة

9 -  an karbo daga baban Abdullah (as) ya ce : wani mtum ya zo wajen manzon Allah (saw) ya ce : ya manzon Allah, an haifa mini da wanne sun azan rada masa ? ka rada masa suna hamza shi ne mafi soyuwa sunaye gareni.

عن أبي عبد الله  (عليه السلام) قال  : قال رسول الله (صلى الله عليه وآله)  : استحسنوا أسماءكم فإنّكم تدعون بها يوم القيامة ، قمّ يا فلان بن فلان إلى نورك ، وقم يا فلان بن فلان لا نور لك

10 – daga baban Abdullah (as) ya ce: manzon Allah (saw) ya ce: kyawunta  sunayenku lalle za'a kiray ku da wadannan sunaye ranar kiyama , ace ta shi wane dan wane babu hske gareka.

عن أبي عبد الله (عليه السلام) قال  : إنّ رسول الله (صلى الله عليه وآله) دعا بصحيفة حين حضره الموت يريد أن ينهى عن أسماء يتسمّى بها فقُبض ولم يسمّها ، ومنها  : الحكم والحكيم وخالد ومالك وذكر أ نّها ستّة أو سبعة ممّا لا يجوز أن يتسمّى بها

11 – daga baban abdullah (as) ya ce: manzon Allah (saw) ya umarci aka masa takarda yayin mutuwa ta gabato masa saboda ya na son hana al'ummarsa sanya wasu sunaye amma sai aka karbi ransa ba tare da ya ambaci wadannan sunaye ba, daga cikinsu akwai hakam da hakim da kalid da malik wasu sunci guda shida zuwa bakwai wadanda bai halasta a rada sunaye da su ba.

عن أبي عبد الله (عليه السلام) أنّ النبيّ (صلى الله عليه وآله) نهى عن أربع كُنى عن أبي عيسى وعن أبي الحكم وعن أبي مالك وعن أبي القاسم إذا كان الاسم محمّداً

12 – daga baban Abdullah (as) cewa annabi ya hana kan alkunya guda hudu daga ciki akwai baban isa, baban hakim, baban maliku, baban kasim idan sunansa muhammadu.

عن أبي جعفر (عليه السلام)  : إنّ أبغض الأسماء إلى الله عزّ وجلّ حارث ومالك وخالد

13 – an karbo daga baban jafar (as) : lalle mafi kiyayyar sunaye wajen Allah mai girma da daukaka sune sunayen haris malik da kalid.

عن زرارة قال  : سمعت أبا جعفر (عليه السلام) يقول  : إنّ رجلا كان يغشى عليّ ابن الحسين (عليهما السلام) وكان يكنّى أبا مرّة وكان إذا استأذن عليه يقول  : أبو مرّة بالباب فقال له عليّ بن الحسين (عليهما السلام)  : بالله إذا جئت بابنا فلا تقولنّ  : أبو مرّة . ( يغشى بمعنى يأتي وأبو مرّة كنية إبليس اللعين ) .

14 –  daga zurara ya ce : na ji baban jafar (as) ya ce: wani mutum ya na zuwan wajen aliyu dan husaini (as) ya kasance ana mai sa alkunya da baban murratu ya kuma kasance idan kai masa iso sai ace baban murratu ya na jiran kofar gida, sai imam ya ce: ina rokonka Allah duk sandfa ya zo ka daina cewa baban murratu ya na jira. lalle baban murratu alkunya ce ta ibilis (la)

عن أبي هارون مولى آل جعدة قال  : كنت جليساً لأبي عبد الله (عليه السلام)في المدينة ففقدني أيّاماً ثمّ إنّي جئت إليه فقال لي  : لم أرك منذ أيّام يا أبا هارون  ؟ فقلت  : ولد لي غلام ، فقال  : بارك الله لك فيه فما سمّيته  ؟ قلت  : محمّداً ، قال  : فأقبل بخدّه نحو الأرض وهو يقول  : محمّد محمّد محمّد ، حتّى كان يلصق خدّه بالأرض ـ  وهذا معنى أنّ الأسماء تذكّرنا بالمسمّيات الرمزيّة في حياتنا  ـ ثمّ قال  : بنفسي وبولدي وبأهلي وبأبوي وبأهل الأرض كلّهم جميعاً الفداء لرسول الله (صلى الله عليه وآله) ، لا تسبّه ولا تضربه ولا تسيء إليه واعلم أ نّه ليس في الأرض دار فيها اسم محمّد إلاّ وهي تقدّس كلّ يوم[2]

15 – daga baban harun bawan alu ja'adatu ya ce: na kasance ina  zama wajen baban Abdullah (as) a madina sai wata rana ya nemi ya rasa , sannan daga bisani na je wajensa, sai ya ce mini: me yasa tsawon kwanaki ban ganka ba baban harun ? sai na ce: an haifa mini yaro ne, sai ya ce:  Allah ya sanya maka albarka cikinsa wanne suna ka sanya masa ? sai na ce: muhammadu, sai ya sunkuyar da kuncinsa zuwa kan kasa ya na ta maimaita muhammadu muhammadu har ma ya goga kuncin kan kasa.

Wannan na nuni da cewa sunan muhamamdu na tunanatar damu da ma'abota wadannan sunaye cikin rayuwar mu – sannan imam ya ce: raina da iyalina da babannina da dukkanin wadanda ke kan kasa fansa ga manzon Allah (saw) ka da ku zage shi ka da ka doke shi ka da ka munana masa ka sani cewa babau wani gida kan kasa da cikinsa akwai muhammadu  face ta tsarkaka kowacce rana.

عن الرضا ، عن أبيه ، عن آبائه (عليهم السلام) ، قال  : قال رسول الله (صلى الله عليه وآله)  : ما من قوم كانت لهم مشورة فحضر معهم مَن اسمه محمّد أو أحمد فأدخلوه في مشورتهم ، إلاّ كان خيراً لهم   

16 – an karbo daga rida (as) daga babansa daga babanninsa (as) ya ce: manzon Allah (saw) ya ce: babu wasu mutane da zaman shawara ya kasance garesu sai wanda sunansa yak e muhammadu ko ahmad ya halarci wannan zama suka shiga da shi cikin shawararsu face alheri yakasance tare da su.

قالوا لأبي طالب  : لأيّ شيء سمّيته أحمد ـ  في تسمية النبيّ (صلى الله عليه وآله)  ـ  ؟ قال  : ليحمده أهل السماء والأرض

17 – an tambayi abu dali abu dalib: saboda me ka rada masa suna ahmad  ? sai ya ce: saboda mutane sama da kasa su dinga gode masa.

الكافي بسنده عن عليّ بن الحكم عن الحسين بن سعيد قال  : كنت أنا وابن غيلان المدائني دخلنا على أبي الحسن الرضا (عليه السلام) فقال له ابن غيلان  : أصلحك الله ، بلغني أ نّه من كان له حمل فنوى أن يسمّيه محمّداً ولد له غلام فقال  : من كان له حمل فنوى أن يسمّيه علياً ولد له غلام . ثمّ قال  : عليّ محمّد ومحمّد  عليّ شيئاً واحداً ، قال  : أصلحك الله إنّي خلّفت امرأتي وبها حمل فادع الله أن يجعله غلاماً ، فأطرق إلى الأرض طويلا ثمّ رفع رأسه فقال له  : سمّه علياً فإنّه أطول لعمره ، وخلنا مكّة فوافانا كتاب من المدائن أ نّه قد ولد له غلام

18 – alkafi da isnadinsa daga ali dan hakam dan husaini dan said ya ce: na kasance ni da dan gilani  almada'ini  mun je wajen aliyu dan husaini (as) sai dan gilani ya ce masa: na samu labara cewa duk wanda matarsa ke da ciki sai yay i niyyar sanya sunan muhammadu to zai sami da namiji, sai ya ce: ali da muhammadu abu guda ne, sai ya ce : Allah ya yi maka gyara lalle ni na baro mata ta da ciki ka roka mini Allah ya sanya shi da namiji, sai imam ya dan sunkuyar da kansa kasa zuwa lokaci mai tsayi sannan ya dago ya ce : ka rada masa suna aliyu lalle hakan zai fi tsawo ga rayuwarsa, sai muka nufi maka sai sako ya zo mana daga garin mada'in cewa an haifa masa da namiji.

Karin bayani cikin cewa ali da muhammadu abu guda ne lalle hadisi ya zo daga annabi (saw) cewa ali daga gareni yak e nima daga gare shi na ke, kamar yadda ya zo cikin fadin sarkin muminai ali (as) : ni daga muhammadu na ke muhammadu daga gare ni ya ke, sune mazharin hakikanin muhammadiya wadda iata wilayar ubangiji ma'abociyar girma.

Hakika himmatuwar muslunci da batun rada sunya ya bayyana karkashin riwayoyin da suka gabata sakamakon tasirin da tattare ga  ruhin yaro, kyakkyawan suna na karfafa ma'abocinsa zuwa ga yanayin da zai dace tare da kyawun sunan, misalin wadda aka rada mata suna fatima lalle wannan suna zai karfafeta zuwa duniyar Fatima azzahara (as) haka al'amarin ya ke kan wadda aka radawa suna maryam ko zainab da yaron da aka rada masa suna muhammadu, aliyu, ahmad  hassan husaini ,

amma wadanda ke da suna irinsu katerin, nirmin, mirfat, hiyam, da makamantansu daga sunayen mata da ke daukar hankalin mai saurare zuwa ga kamaceceniya cikin ma'ana wadannan sunaye haka al'amarin yak e ga sunayen maza misalin sumairi ko azab.

zamu sami muslunci ya dau matsaya tsatstsaura kan miyagun lakubba wadanda ke bayyana kaskanci ga ma'abocinsu, wannan zamani namu da muke ciki cike yak e da ire iren wadannan miyagun lakubba musammam ma cikin kauyuka da karkara ta yadda cikin gaggawa za ka samu yaro ya damfaru da wani mugun lakabi da zai ta bin zuriyarsa har ranar kiyama.

na tuna da wata kissa da kea da alaka da maudu'in mu, wani bako ya sauka wurin wasu mutane da suke da wani karamin yaro da ke suna Ibrahim mai yawan kazar kazar da kiriniya mahaifinsa ya kasance ya ne masa lakabi dabbur ma'ana kudan zuma sai abokin mu ya nuna masa bacin ransa kan wannan lakabi ya gaya masa illolinsa da irin cutarwar da zai wa yaron ya nuna masa cewa wannan lakabi zai dinga bin yaron har zuwa girmansa da kuma bin zuriyarsa, duk sand aka gansu sai ace ai wane jikan wane dabbur wanda hakan zai cutar da dukkaninsu, daga karshe ya bashi shawara da nasiha kan ya daina kiransa da wannan mugun lakabi, sai mhaifin yaron ya wakilta wannan abokin namu da yasaya masa da alkunya sai ya sanya masa alkunya da baban Khalil, bayan shudewa shekara sai wannan aboki na mu kara zuwa wajen mahaifin yaron ya tambaye shi kan yarjejeniyarsu, sai mahaifin ya amsa da cewa: mu dai kadai muna aiki da yarjejeniya idan mun yarda da yaro sai mu kiraye shi da baban Khalil, amma duk lokacin da muka ga yana kiriniya sai mu kira shi da dabbur.

الكافي بسنده عن معمر بن خيثم قال  : قال لي أبو جعفر (عليه السلام)  : « ما  تُكنّى  ؟ » قال  : قلت  : ما اكتنيت بعد وما لي ولد ولا امرأة ولا جارية ، قال  : فما يمنعك من ذلك  ؟ قال  : قلت  : حديث بلغنا عن عليّ (عليه السلام) . قال  : وما هو  ؟ قلت  : بلغنا عن عليّ (عليه السلام) أ نّه قال  : من اكتنى وليس له أهل فهو أبو جعر ـ  ما ييبس من الثقل في الدبر أو خرج يابساً  ـ فقال أبو جعفر (عليه السلام)  : شوّه ـ  كلمة نفرة  ـ ليس  هذا من حديث عليّ (عليه السلام) ، إنّا لنكنّي أولادنا في صغرهم مخافة النبز أن يلحق بهم ـ  النبز أي اللقب السوء

19 – alkafi da isnadinsa daga mu'ammar dan kaisam ya ce : baban jafar (as) ya ce mini: da me kuke alkunya, sai na ce ban yi alkunya ba saboda banda da banda mata banda kuyanga, sai ya ce: me ya hana yin haka ? sai na ce saboda wani hadisi da ya zo mana daga ali (as) sai y ace wanne ne ? sai na ce: mun samu labara cewa ali (aas) ya ce: duk wand ya yi alkunya alhalin bai da iyali to lalle shi baban ja'aru ne () sai ya ce: wannan baya daga zancen ali (as) lalle mu muna sanyawa `ya`yanmu alkunya tun suna kanana saboda gudan ka da miyagun lakubba su riske su.



[1] Alwafi m 12 sh 1327

[2] Alwafi m 12 sh 1327